Skip to main content

fassarar waqen ‎بداية السول في تفضيل الرسول صلى الله عليه وآله وسلم للشيخ العلامة العز عبد العزيز بن عبد السلام السلمي"

HIMMA BATA GA RAGO!

Waƙe kenan na Littafin:

"بداية السول في تفضيل الرسول صلى الله عليه وآله وسلم للشيخ العلامة العز عبد العزيز بن عبد السلام السلمي".

Wanda wani ɗalibi cikin ɗalibai na Markazul Wa'ayil Islamiy Tudun Jukun Zaria, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Basheer Lawal Muhammad Zaria ya tsarasu a matsayin ta shi gudumuwar; don bada kariya ga Manzon tsira (S.A.W).

Ɗalibi mai suna: Imrana Hamza 👳🏻‍♂️

1. Ya wanda ba shi da kishiya,
     Mata kaza ɗa bai da shi.

2. Shi ke da mulkin duniya,
     Al'arshi shi ɗai ke da shi.

3. Tsira, Aminci, ɗaukaka,
     Gun wanda babu awa ya shi.

4. Alai da matayensa duk,
    Har mai biyar su ka sa da shi.

5. Ka daɗan basira Rabbana,
     Waƙe na ɗan rera wa shi.

6. Shi ne ka aiko gunmu duk,
    Ɗa'a ka ce mu yi yo ga shi.

7. Ka ba shi duk matsayan da ba,
   Wani wanda yai dai dai da shi.

8. Ya zarce kowa duniya,
     Har Lahira an san da shi.

9. Aikensa ya game ko'ina,
    Ba wanda zai ce ban da shi.

10. In za a ceto Lahira,
      Tilas a dangantaka da shi.

11. Shi ke da Tutar godiya.
     A cikinta har Adam da shi.

12. Zunubi idan ma za ya yi,
      Tuni Rabbi yai Afuwa ga shi.

13. Ƙaunarsa wadda yake mana,
      Ta zarce nasa da kansa shi.

13. Har addu'a aka ba shi ma,
     Amma tunani ne da shi.

14. Ya ƙi yi wa kansa ya bar mana.
     Ya san nufar da yake da shi.

15. Sai ran da rana za ta ɓa-,
     Ci, ya ce a ɗan amsa wa shi.

16. Domin ya sam cetonmu duk,
     Aljanna duk mu shige da shi.

17. Kuma Rabbana na ji da shi,
     Domin ko bai da awa ya shi.

18. Rayuwarsa ya rantse da shi,
     Albarkacin da take da shi.

19. Kuma bai kiran sunansa sam,
    Haka girmamawa ce ga shi.

20. Haka nan da Ƙur'aninsa ma,
     Har gobe na aiki da shi.

21. Ya zam mafi girman abin,
    Gasar da kaf ba mai ya shi.

22. Dutse yana masa sallama,
    Sannan  yana gaishe da shi.

23. Yatsunsa sun tsatso ruwa,
      Har an yi alwalla da shi.

24. Haka ya mayar da idaniya, 
    Bayan fitar ijiya a shi.

25. Ya raya dubban jikkuna,
      Zucinsu sam ba rai a shi.

26. Zai sami sakamako na duk,
   Ladaddakin da muke da shi.

27. Duk ayyukanmu da munka yi,
    Sanadinsa ne muka san da shi.

28. Duk Annabin da ya zo a da,
    Jama'arsa ɗai suka san da shi.

29. Shi ko gamewa anka yi,
    Duka duniyar aka bai wa shi.

30. Musa da yai zance da shi,
  A kwarin Ɗtuwa aka yo da shi.

31. Shi sanda an ka yi yo da shi,
      Ai can Sama'u a kai da shi.

32. Jama'arsa ce ƙarshen zuwa,
    Amma Ƙiyama fari shi.

33. Mu za a fara kira a can,
     Farkon shiga Aljanna shi.

34. Duka Annabawa za su so,
    Da ma a ce su ne a shi.

35. Shi za ya fara fita ƙasa,
   Domin Hisabi sai da shi.

36. Haka ma Wasila tashi ce,
     Ya Rabbana ka isar ga shi.

37. Jama'a dubu saba'in ku san,
   Aljanna za su shige da shi. 

38. Kuma ba hisabi ko kaɗan,
     Ba zai Uƙubantar da shi.

39. Tafkinsa shi ɗai ke da  shi. 
     Alkauthara aka bai wa shi.

40. Haka an halasta mai gani-,
  Ma, don irin matsayinsa shi.

41. An bar ƙasa mu yi Taimama,
     Salla ya ce mu yi yi a shi.

42. Kyawun ɗabi'a ke da shi,
    Har Jalla ya yi yabo ga shi.

43. Allahu yai magana da shi,
    Da dukan salon da yake da shi.

44. Wahayi da Ilhama duka,
    Busa, mafarki yai da shi.
 
45. An ba shi littafin da ba-, 
    Bu, irinsa wanda yake da shi.

46. A cikinsa kwai Taura da In-,
   Jila, Zabura kwai a shi.

47. Ya ƙunshi nasu gaba ɗaya,
     Su nasu bai tsara da shi.

48. Aikinmu ya zam ɗan kaɗan,
    Ladansa ba dai dai da shi.

49. An ba shi zaɓi don ya zam,
    Sarkin da babu awa ya shi.

50. Ko ko ya zamto Annabi,
    Bawan da babu irin sa shi.

51. Jibrilu sai yac ce da shi,
     Ce ka zame Bawa ga shi.

52. Haka sai ya ba shi Tagomashi,
    Ya zamo mutum mai Arashi.

53. Sai Rabbi yai masa lamuni,
   In an yi Imanin da shi.

54. Halaka ba zai riske mu ba,
     Matuƙar muna ɗa'a ga shi.

55. In za ka san shi haƙiƙani,
   Je duba Ƙur'aninsa shi.

56. Sauƙin hali ne ke da shi,
    Ba wanda ke kuka da shi.

57. Kaushinsa ya fi ga Kafirai,
   In sun ƙi amsa kiransa shi.

58. Bai son tsanantawa ga mu,
    Don ya fi sonmu a kansa shi.

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

Magungunan Musulunci Fitowa Ta farko

HABBATUS-SAUDA: Daga Nana A'isha (RA) ta ce: "Manzon Allah (SAW) ya ce: wannan Habbatus-Sauda waraka ce daga dukkan cuta sai dai mutuwa. FA'IDOJINTA: Idan aka damqata aka dama da zuma aka sha da ruwa mai zafi tana narkar da tsakuwar ciki. Tana vuvvugar da fitsari da haila da nono, idan aka sha zuwa kwana biyu. Tana maganin kuturta. Tana amfani wajen rage majina. Ana dandaqata a zuba a wani qyalle a shaqa don maganin ciwon kai nan take, da mura. Shan ta da ruwa yana da amfani ga mai numfashij da qyar. Don haka tana matuqar taimakawa mai Asma. Hakanan mun tato sinadaranta mun zuba a wani magani mai suna (TASIRI DAGA ALLAH), don haka za ku iya neman wannan magani. ARRAIHAN/XOXXOYA Raihan tsiro ne mai qamshi, ana shuka shi a kudancin Asiya da Iran da wani vangare na Africa da tsakiyar America. Allah (S.W.T) yana cewa: " ﻓﺄﻣﺎ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻘﺮﺑﻴﻦ * ﻓﺮﻭﺡ ﻭﺭﻳﺤﺎﻥ ﻭﺟﻨﺔ ﻧﻌﻴﻢ " Amma wanda ya kasance daga cikin makusanta hutu da bishiyar Raihan da Aljanna sun tabbata a gare sh...

amfani da maganin tazarar haihuwa wato implan

  MAGANIN RIKICEWAR JININ HAILA : TAMBAYA TA 2282 ******************* Assalam, malam dan Allah sakaye sunana. Yaya aiki? Malam nice nake amfani da maganin tazarar haihuwa wato implan yanzu wata na hudu kenan, to kwanan nan se ya fara min wasa da al'ada ta, se nayi sati biyu ya dawo wannan karon kam ma bekai sati daya ba ya dawo, naga yadan zubo se kuma ban gani ba kuma a wannan rana ina azumi shin malam menene hukuncin sallah ta da azumi na? Shin wannan jini ya zama na ciwo ne ko kuma? Domin an bani magani a asibiti domin ya gyara min. Malam ayi hakuri zanso a tura min amsar ta nan. Nagode. AMSA ******* Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu. Su kwayoyi ko alluran tazarar haihuwa sukan yi kokarin chanza yanayin halittar Mace ne daga ainahin ginin farko wanda Ubangiji ya halicceta akansa. Don haka dole arika samun matsaloli marassa adadi. Mafiya yawan Matayen dake shiga wannan tsarin sai, sun sha fama da rikicewar jinin Al'ada. Wasu ma ciwuka da jinyoyi kala-kala a sassa...

Haila

  Haila Bayanin menene haila Kalmar (Haila) a larabci Tana nufin Kwararar wani abu da gudanar shi Ma’anar (Haila) a shari’a Wani jini ne da yake fita daga mahaifar mace, a wasu lokuta sanannu, ba tare da wani dalili ba. Siffar Yadda Jinin Haila Yake Baqi ne wuluk, kamar wanda aka qona, warinsa bai da daxi, mace tana jin xumi mai tsanani idan ya zo. Shekarun Fara Jinin Haila Babu wasu shekaru qayyadaddu na fara al’ada, wannan ya danganta ne da savanin xabi’ar mace da inda take rayuwa da yanayin wajen, don haka duk lokacin da mace ta ga jinin haila to haila ce. Tsawon Lokacin Haila Haila ba ta da wani lokaci, sananne, cikin mata akwai masu yin kwana uku, akwai masu kwana huxu. Galibin haila dai kwana shida ne ko bakwai, saboda faxin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ga Hamnatu ‘yar Jahshin – wanda ta kasance tana yin haila kwanaki masu yawa –  “Ki yi haila kwana shida, ko bakwai, da ilimin Allah, sannan ki yi wanka”  [Abu Dawud ne ya rawaito shi] Mas'aloli 1 - A qa'ida ma...