*HADISI DA SUNNAH*
*(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*
Rubutun
Muhammad Abdullaah Assalafiy
_(Abu-Abdillaah)_
*Darasi na 03*
*SUNNAH DAIDAI DA ALƘUR’ANI TA KE*
Sanannen abu ne a wurin dukkan *Ahlus-Sunnah* cewa Alƙur’ani maganar Allaah ne, saukakke daga wurinsa ba halitacce ba ne, wanda kuma Allaah ya bautar da bayi da karatunsa. Shi wata wanzajjiya kuma tabbatacciyar mu’ujiza ce da ta gagari dukkan halittu a kan su zo da irinta!
Ta wannan fuskar Alƙur’ani a sama ya ke, kuma ya fi falala da daraja a kan dukkan maganganun da ba shi ba, har da Sunnar Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)._
Amma ta fuskar kafa hujja ko fitar da dalili a kan wani hukuncin shari’ah, Sunnah Sahihiya daidai ta ke da Alƙur’ani, babu fifiko a tsakaninsu. Domin dai dukkansu wahayi ne daga wurin Allaah Maɗaukakin Sarki wanda ya faɗa game da Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam):_
وَمَا یَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰۤ . إِنۡ هُوَ إِلَّا وَحۡیࣱ یُوحَىٰ
Kuma ba ya yin furuci daga sha’awar rai, (maganarsa) ba komai ba ce sai dai wahayi kawai da ake yi masa. _Suratun Najmi: 3-4_
Kuma malamai sun nuna cewa:
كَانَ جِبْرِيلُ عَلَيْهِ السَّلَامُ يَنْزِلُ عَلَى النَّبِيِّ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَآلِهِ وَسَلَّمَ - بِالسُّنَّةِ ، كَمَا يَنْزِلُ عَلَيْهِ بِالْقُرْآنِ
Mala’ika Jibril _(Alaihis Salaam)_ yana sauka ga Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ da wahayin Sunnah, kamar yadda yake sauka gare shi da wahayin Alƙur’ani.
_(Al-Imaam Ad-Daarimiy (lamba: 608) ya riwaito shi daga Hassaan Bn Atiyyah. Kuma Hussain Salim Asad Ad-Daaraaniy mai tahaƙiƙin littafin, bayan ya kawo riwayoyinsa da yawa daga Hassaan sai ya ce (1/474): Isnadinsa Sahihi ne)._
Don haka, babu shakka! Babban kuskure ne, kuma ko kaɗan ba daidai ba ne: Abin da waɗansu malamai suka gudana a kansa na fifita Alƙur’ani a kan Sunnah a wurin kafa hujja, ko fitar da wani hukuncin shari’a.
Babban dalilinsu a kan hakan kuwa shi ne: Hadisin Mu’azu Bn Jabal _(Radiyal Laahu Anhu)_ cewa wai:
A lokacin da Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya aiki shi Mu’azun zuwa ƙasar Yamen sai ya ce da shi: Da me za ka yanke hukunci idan aka kawo maka ƙara?
Sai Mu’azu ya ce: Zan yi hukunci ne da abin da yake cikin Littafin Allaah!
Ya ce: Idan kuma ba ya cikin Littafin Allaah fa?
Sai ya ce: Sai in yanke da Sunnar Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)!_
Ya ce: In kuma ba ya cikin Sunnar Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ fa?
Sai ya ce: Sai in yi ijtihadi da ra’ayina, kuma ba zan yi sakaci ba!
A nan ne wai sai Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya dafa ƙirjinsa, kuma ya ce:
« الْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذِى وَفَّقَ رَسُولَ رَسُولِ اللَّهِ لِمَا يُرْضِى رَسُولَ اللَّهِ »
Godiya ta tabbata ga Allaah Wanda ya datar da ɗan saƙon Manzon Allaah ga abin da Manzon Allaah yake yarda da shi.
_(Hadisi ne Da’eef. Manyan Malaman Hadisi irin su Al-Bukhaariy da At-Tirmiziy da Al-Uqailiy da Ad-Daaraqutniy da Ibn Hazm da Ibn Taahir da Ibn Al-Jawziy da Az-Zahabiy da As-Subkiy da Ibn Hajr duk sun raunana shi. Lallai ka karanta Silsilah Da’eefah: 2/273-286 domin samun natsuwa, ka rabu da hayaniyar waɗanda ba su gama nuna ba)._
Sai dai kuma tun tuni malamai muhaƙƙiƙai sun tabbatar da cewa wannan ba hujja ba ce!
Saboda me?
Domin da farko dai wannan hadisin da’eef ne mai rauni, wanda kuma ba a iya kafa hujja da shi *ittifaaqan* , musamman a kan al’amarin addini mai girma irin wannan: Watau al’amarin fitar da hukuncin Fiqhu daga cikin nassoshi.
Sannan kuma kamar yadda malamai suka faɗa, yin amfani da koyarwar da ke cikinsa yana sanyawa a tafka mummunan kuskure a wurin yanke hukunci a cikin mas’aloli masu yawa.
Alal misali: Idan aka yi fatawa ga mutumin da yake tafiya a kan koyarwar wannan hadisin cewa: Menene hukuncin mataccen kifi?
Abin da zai fara tunowa a cikin Alƙur’ani ita ce Ayar da ta ce:
حُرِّمَتۡ عَلَیۡكُمُ ٱلۡمَیۡتَةُ وَٱلدَّمُ وَلَحۡمُ ٱلۡخِنزِیرِ
An haramta muku cin mushe da jini da naman alade. _Suratul Maa’idah: 3._
Har zuwa ƙarshen Ayar.
A kan haka zai iya yanke hukunci da cewa: Mataccen kifi ma haram ne!
Daga nan, ka ga sai ya tafka mummunar ɓarna!! Ya haramta wa musulmi daddaɗan nama mai lafiya wanda Allaah Ta’aala bai haramta musu ba!
Me ya kai shi ga haka?
A saurari zuwan *darasi na 04* _in shaa'al Laah_ .
Comments
Post a Comment