*HADISI DA SUNNAH*
*(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*
Rubutun
Muhammad Abdullaah Assalafiy
_(Abu-Abdillaah)_
*Darasi na 05*
*SUNNAH A CIKIN ALƘUR’ANI*
A cikin Ayoyi masu yawa na Alƙur’ani Allaah Mabuwayi Mai Girma ya bayyana matsayin Sunnah a cikin Musulunci, kamar inda ya ce:
*Aya ta ɗaya:*
وَأَنزَلۡنَاۤ إِلَیۡكَ ٱلذِّكۡرَ لِتُبَیِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَیۡهِمۡ وَلَعَلَّهُمۡ یَتَفَكَّرُونَ
Kuma mun saukar da Alqur’ani a gare ka ne domin ka yi wa mutane bayanin abin da aka sassaukar musu, kuma domin ko sa riƙa yin tunani. _(Suratun Nahli: 44)._
Wannan aya ta nuna:
(i) Babban aikin da Allaah _(Subhaanahu Wa Ta’aala)_ ya ɗora wa Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ shi ne yin bayanin Alqur’anin da ya saukar masa.
(ii) Haƙiƙa! Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya bi wannan umurnin na Allaah _(Subaanahu Wa Ta’aala):_ Ya yi cikakken bayanin Alƙur’anin har na tsawon shekaru ashirin da uku.
(iii) Ya bi hanyoyi uku wurin wannan bayanin: Ta hanyar bayanin da bakinsa, da hanyar yin aiki da gaɓoɓinsa, da kuma hanyar tabbatarwa ga ayyuka ko maganganun da Sahabbansa _(Radiyal Laahu Anhum)_ suka yi a gabansa.
(iv) Kuma wannan bayanin shi ne malaman Sunnah da Hadisi - Allaah ya saka musu da mafi kyawun alkhairinsa - suka tattara a cikin Littaffan da ake kira *Littaffan Sunnah* ko *Hadisi* .
Watau: Littaffai irin su: *Sihaah* da *Jawaami’* da *Sunan* da *Masaanid* da *Ma’aajim* da *Mustadrakaat* da *Mustakhrajaat* da *Ajzaa’* da sauransu na nau’ukan wallafe-wallafe masu daraja da ƙima da girma na manyan Malaman Hadisi da Sunnah. _(Dubi Makaanatu Ahlil-Hadeeth)._
(v) Kuma idan ba ta bin Sunnah ba ta yaya saƙon Allaah da ke cikin Alƙur’anin zai bayyana ga al’umma har su iya haɗuwa a kan yin aiki da shi kamar yadda Allaah yake so?!
Allaah ya ƙara mana shiriya.
*Aya ta biyu:*
وَمَاۤ ءَاتَىٰكُمُ ٱلرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَىٰكُمۡ عَنۡهُ فَٱنتَهُوا۟ۚ وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِیدُ ٱلۡعِقَابِ
Kuma abin da Manzon ya ba ku sai ku karɓe shi, kuma abin da ya hane ku sai ku hanu, kuma ku ji tsoron Allaah. Lallai Allaah mai tsananin uƙuba ne. _(Suratul Hashri: 7)_
Wannan ya nuna:
(i) Allaah Maɗaukaki Mai Girma doka yake ba mu bayinsa, yake yi cewa: Duk mu maƙalƙale wa Sunnar Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)._
(ii) Ana bin Sunnar ce kuwa ta kama yin aiki da abin da Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallaam)_ ya kawo, da barin duk abin da ya hana.
(iii) Allaah yana tsawatar da mu cewa: Kar mu yarda mu ƙi bin Sunnah a cikin komai, kar kuma mu kuskura mu yi ƙoƙarin yin watsi da ita.
(iv) Sannan masu irin wannan tunanin na ƙin bin Sunnah a cikinmu: Su ji tsoron Allaah, kar su yi sakaci har Allaah ya kama su da laifin saɓa wa umurninsa ko haninsa.
(v) Domin kuwa shi mai tsananin uƙuba ne ga dukkan wanda ya yi ƙarfin halin saɓa masa, ya aikata abin da ya hana shi aikatawa a kan harshen Manzonsa _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)._
..........................
A saurari zuwan *darasi na 06* _in shaa'al Laah._
Comments
Post a Comment