IBNU TAIMIYYA YA FI KOWA RADDI WA 'YAN BIDI'A, AMMA KUMA DUK DA HAKA YA FI KOWA YI MUSU UZURI DA ADALCI
Abu ne sananne Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya (r) yana daga cikin Imaman Ahlus Sunna wal Jama'a, wanda a bayansa har zuwa yau ba a samu wanda ya kai shi girmamawa da bin Nassoshin Al- Qur'ani da Sunna da Tafarkin Salaf (magabata) ba.
Wannan ya sa ba a samu wanda yake kare Sunna da tafarkin magabata kamarsa ba, shi ya sa ya fi kowa raddi ma wadanda suka saba tafarkin Annabawa, tun daga kan 'Yan Falsafa, Mulhidai, Mushrikai da Majusawa, Yahudawa da Kiristoci da dukkan dangogin kungiyoyin 'yan bidi'a.
Amma abin mamaki, duk da haka ya kasance mutum ne mai adalci saboda binsa ga Al- Qur'ani da Sunna da tafarkin Salaf, shi ya sa ba ya yin kudin goro wajen yanke hukuncinsa ga 'yan bidi'a, a'a, kowa yana yi masa hukunci ne gorgodon girman bidi'arsa da halinsa na bin son rai ko kuskure, wanda kuma yake bukatar azuri yana yi masa uzuri tare da yi masa fatan samun gafara a kan kuskuren nasa.
Ibnu Taimiyya yana magana a kan wadanda suka hada ra'ayin "hululi" (Allah ya shiga cikin halitta) da rabuwansa da halittan (الذين يجمعون بين الحلول والمباينة) a cikin maganarsu a game da Allah (T), sai yake yin uzuri ma wasu daga cikin Shehunai Sufaye masu ilimi da suka yi kuskure aka samu irin wadannan munanan maganganu a cikin maganganunsu, sai ya ce:
لكن شيوخ أهل العلم الذين لهم لسان صدق وإن وقع في كلام بعضهم ما هو خطأ منكر فأصل الإيمان بالله ورسوله إذا كان ثابتا غفر لأحدهم خطأه الذي أخطأه بعد اجتهاده
الصفدية (1/ 265)
"Sai dai Shehunai masu Ilimi, wadanda suke da kyakkyawan ambato a cikin al'umma, ko da an samu abin da yake mummunan kuskure ne da ya faru a cikin maganganun wasu daga cikinsu, to asalin Imaninsu da Allah da Manzonsa, idan ya kasance tabbatacce (a cikin addininsu), Allah zai gafarta ma kowane dayansu kuskurensa da ya yi a bisa Ijtihadinsa".
Wannan shi yake nuna mana cewa; Shugabanni a cikin Sunna, sun fi kowa Ilimi da Adalci, suna banbance wanda ya afka cikin bidi'a bisa son rai, suna banbance wanda ya yi bidi'a da kuskure, balle kuma wanda ya yi a bisa Ijtihadi, shi kam ana yi masa fatan samun lada a kan Ijtihadin nasa.
Lallai hukunci da bidi'a wa mutane yana da wahala, sabanin yadda a yau abin ya zama a hanun dukkan wanda ya ga dama.
Allah ya yi mana afuwa, ya kiyayemu.
Rubutawar: Dr. Aliyu Muh'd Sani
Comments
Post a Comment