Kasancewar hakikanin Falsafa shi ne dogaro a kan hankali zalla wajen sanin hakikanin lamura da yi musu hukunci, in mun duba za mu ga Iblis shi ne farkon wanda ya fara zuwa da Nazariyyar gabatar da hankali a kan komai wajen yanke hukunci. Ya yi amfani da wannar Nazariyya ce (theory) inda ya gabatar da hankalinsa a kan maganar Allah Madaukaki ya yanke hukunci da ya saba umurnin Allah.
Hakan ya faru ne a lokacin da Allah ya umurce shi da yin Sujada ga Annabi Adamu (as), sai ya kalubalanci Allah da wata ka'ida ta Falsafa mai doriya biyu kamar haka:
1- Ni da wuta ka halicce ni, shi kuma (Annabi Adamu) da tabo ka halicce shi, wuta kuwa ta fi tabo daraja.
2- Don haka wanda aka halicce shi da wuta ya fi wanda aka halicce shi da tabo daraja.
Natijar wannar Qadhiyya ita ce: Ni na fi Adamu daraja, don haka ni ba zan yi masa sujada ba.
Shi ne inda Allah ya ba mu labarin wannan (Logic) na Philosopher Iblisu inda ya ce:
{قَالَ مَا مَنَعَكَ أَلَّا تَسْجُدَ إِذْ أَمَرْتُكَ قَالَ أَنَا خَيْرٌ مِنْهُ خَلَقْتَنِي مِنْ نَارٍ وَخَلَقْتَهُ مِنْ طِينٍ } [الأعراف: 12]
"Allah ya ce: me ya hana ka ba za ka yi sujada ba, a yayin da na umurce ka? sai (Iblis) ya ce: Ni na fi shi daraja, saboda ka halicce ni da wuta, shi kuma ka halicce shi da tabo".
To a nan in ka lura za ka ga wannan tsohon wato Iblisu, ya gabatar da hankalinsa da ra'ayinsa a kan Nassi bisa dogaro ga Nazariyyar Falsafa.
Saboda haka, kalubalantar Allah da Manzonsa da gabatar da hankali da ra'ayi da Nazariyya ta Falsafa a kan maganar Allah da Manzonsa gado ne daga Philosopher Iblisu kakan 'Yan Falsafan farko.
Wannan ya sa Philosopher Iblisu bai gushe ba a kullum yana wahayi ga almajiransa magada Falsafarsa da cewa; ku yi jayayya ga masu riko da Aya da Hadisi, ku kure su da Nazariyyar Falsafar da na koya muku, Allah ya ce:
{وَإِنَّ الشَّيَاطِينَ لَيُوحُونَ إِلَى أَوْلِيَائِهِمْ لِيُجَادِلُوكُمْ وَإِنْ أَطَعْتُمُوهُمْ إِنَّكُمْ لَمُشْرِكُونَ } [الأنعام: 121]
Da wannan za ka fahimci cewa; lallai Falsafa gado ce daga Philosopher Iblis, wanda ya fara aiki da Nazariyyar gabatar da hankali a kan maganar Allah Madaukaki da Annabawansa. Saboda kowa ya san cewa; Falsafa ta ginu ne a kan girmama hankali da gabatar da shi a kan komai daga cikin hanyoyin sanin abubuwa da yanke musu hukunci.
Saboda haka Iblis shi ne Philosopher na farko, shi ne babban Shehin 'Yan Falsafa gaba daya, kuma kakansu.
Rubutawar: Dr. Aliyu Muh'd Sani
Comments
Post a Comment