WAJIBI NE MU NISANCI DUK ABIN DA ZAI JANYO KIYAYYA A TSAKANIN AHLUS SUNNA
Imamu Muslim ya ruwaito:
عن أنس، أن النبي صلى الله عليه وسلم، قال: «لا تحاسدوا، ولا تباغضوا، ولا تقاطعوا، وكونوا عباد الله إخوانا»
صحيح مسلم (4/ 1983)
"Kar ku yi Hasada a tsakaninku, kar ku yi Kiyayya a tsakaninku, kar ku yanke alaka da juna, ku zama bayin Allah 'yan uwan juna".
Shaikhul Islam ya ce:
وقرن في الحديث الأول الحسد بالبغضاء؛ لأن الحاسد يكره أولا فضل الله على ذلك الغير؛ ثم ينتقل إلى بغضه؛ فإن بغض اللازم يقتضي بغض الملزوم فإن نعمة الله إذا كانت لازمة وهو يحب زوالها وهي لا تزول إلا بزواله أبغضه وأحب عدمه والحسد يوجب البغي كما أخبر الله تعالى عمن قبلنا: أنهم اختلفوا من بعد ما جاءهم العلم بغيا بينهم فلم يكن اختلافهم لعدم العلم بل علموا الحق ولكن بغى بعضهم على بعض كما يبغي الحاسد على المحسود.
مجموع الفتاوى (10/ 127)
"Annabi (saw) ya hada tsakanin Hasada da Kiyayya a cikin Hadisin farko, saboda farko mai hasada yana kin falalar da Allah ya yi ma waninsa ne, sai kuma ya tashi daga hasada zuwa kiyayyar mutumin, saboda kin "lazimi" yana hukunta kin "malzumi", saboda idan ni'imar Allah ta kasance ta lazimci wani mutum, sai shi kuma yake so ta gushe, alhali ba za ta gushe ba sai mutumin da kansa ya gushe to zai ki shi, kuma ya so a rasa mutumin.
Haka kuma Hasada tana haifar da zalunci kamar yadda Allah ya ba da labari game da wadanda suka gabace mu, cewa; sun yi sabani bayan ilimi ya zo musu saboda zalunci a tsakaninsu, don haka sabaninsu bai kasance saboda rashin ilimi ba, a'a, sun san gaskiya amma sai sashe ya zalunci sashe, kamar yadda mai hasada yake zaluntar wanda yake yi wa hasada".
ABIN LURA:
1- Wajibi ne a kan dukkan bangarori na Ahlus Sunna da daidaikunsu su cire hasada wa juna daga cikin zukatansu.
2- Hasada ce take janyo kiyayya da zalunci a magana ko aiki, daga nan kuma sai kaurace wa juna da rabuwar kai.
3- Sabani a kan kananan mas'alolin Addini irin mas'alolin Sadalu da Qabdhu, da makamantansu, ba ya kai wa ga kiyayya da zalunci a magana ko aiki da rabuwar kai.
BA ZA MU SAMU HADIN KAI A TSAKANINMU BA SAI MUN NISANCI HASADA DA DUKKAN ABIN DA ZAI JANYO KIYAYYA DA ZALUNCI A TSAKANINMU.
Comments
Post a Comment