Skip to main content

YADDA MUSULMI ZAI KUNYATA YAHUDU DA NASARA DA 'YAN SHI'A

 YADDA MUSULMI ZAI KUNYATA YAHUDU DA NASARA DA 'YAN SHI'A

Wata Tattaunawa ta gudana tsakanin wani Musulmi da wani Bayahude a Birnin Basra ta Kasar Iraki. Bayahuden ne ya fara tambayar Musulmin.
Bayahude ya ce:
Annabi Musa (as) Annabi ne cikin Annabawan Allah, kuma Annabtarsa gaskiya ce, ta tabbata da dalilai da hujjoji, to shin ka yarda da wannan, ko kuma a'a ba ka yarda ba?
Musulmi ya ce:
Amsar tambayarka za ta kasance ne ta fiska biyu kamar haka:
1- Annabi Musan (as) da ya ba da tabbacin Annabtar Annabi Muhammad (saw), kuma har ya yi umurni da yin Imani da shi da binsa, har ya yi bushara da shi da Annabtarsa, wannan Annabi Musan (as) na yi Imani da Annabtar.
Don haka idan wannan Annabi Musan (as) kake nufi, to ko shakka babu na yarda da shi, kuma na yi Imani da shi.
2- Amma idan kuma kana tambayana ne a kan Musan da bai yarda da Annabtar Annabi Muhammad (saw) ba, kuma bai yi umurni da binsa ba, bai yi bushara da shi ba, to ni ban san wannan Musan ba, kuma ban yarda da Annabtarsa ba. Kai, ni a wajena wannan Shaidani ne.
Nan da nan sai Bayahude ya rude, ya rasa me zai ce.
Sai ya sake yi masa tambaya.
Bayahude ya ce:
To me za ka ce a game Littafin Attaura?
Musulmi ya ce:
Amsar tambayarka ta fiska biyu ce kamar haka:
1- Idan Littafin Attaura da aka saukar wa Annabi Musa (as), wacce a cikinta take tabbatar da Annabtar Annabi (saw) to Attaurar gaskiya ce, na yi Imani da ita.
2- Amma idan kuma Attauran da kake magana a kanta, ba ta yi Bushara da Annabi Muhammad (saw) ba, to ba gaskiya ba ce, kuma ban yi imani da ita ba.
Karshe Bayahude ya rasa abin fada, sai ya ce: Ina son ganinka, sai da suka kebe gefe, ya dauka abin kirki zai fada masa, sai ya zo kusa da kunnensa, sai ya ce: Uwarka kaza da kaza... Ya dura masa ashar...
To haka dai Bayahude ya yi girman kai, ya rufe da zagi da cin mutunci.
To haka ake yin Mujadala, ta hanyar tambaya da Istifsari.
Saboda haka idan ka fahimci wannan, to haka za ka yi wa Banasare idan tattaunawa ta hada ka da shi.
Haka Dan Shi'a ma a game da Sayyidina Aliyu (ra).
Idan Dan Shi'a ya ce maka:
Imam Aliy (as) shi ne dan uwan Annabi (saw), kuma mijin Fatima (ra), wacce tsoka ce daga Annabi (saw), kuma wanda yake a wajen Annabi (saw) a matsayin Annabi Haruna (as) a wajen Annabi Musa (as), ka yarda da shi a matsayin Imami da Khalifa bayan Annabi (saw) kai tsaye, ko kuma ba ka yarda ba?
Kai kuma Ahlus Sunna sai ka ce masa:
Amsar tambayarka ta fiska biyu ce kamar haka:
1- Wannan Aliyun da kake magana a kansa, idan shi ne Sayyidina Aliyu (ra) wanda ya yarda da Khalifancin Abubakar (ra) da Umar (ra) da Usman (ra), yake daukarsu a matsayin 'yan uwansa a Addini da Imani, kuma shugabanninsa, har ya yi Mubaya'a ma kowannensu, kuma yake a matsayin Wazirinsu, kuma shi ne Khalifa na hudu a bayansu, har yake cewa: Duk wanda ya gabatar da ni a kan Abubakar da Umar sai na yi masa haddin Kazafi, to na yarda da wannan Aliyun (ra), kuma ina sonsa.
2- Amma idan kuma kana nufin shi ne Aliyun da bai yarda da Khalifancin Abubakar da Umar da Usman ba, har yake cewa shi ne Khalifa Imami a bayan Annabi (saw) kai tsaye ba tare da maraba ba, kuma yake daukarsu a matsayin azzalumai 'yan fashin Khalifanci fasikai, ko kafirai to ban san wannan Aliyun ba, kuma ban yarda da khalifancinsa ba, kuma ba ruwana da shi, kuma fitinanne ne kawai.

Comments

Popular posts from this blog

Magungunan Musulunci Fitowa Ta farko

HABBATUS-SAUDA: Daga Nana A'isha (RA) ta ce: "Manzon Allah (SAW) ya ce: wannan Habbatus-Sauda waraka ce daga dukkan cuta sai dai mutuwa. FA'IDOJINTA: Idan aka damqata aka dama da zuma aka sha da ruwa mai zafi tana narkar da tsakuwar ciki. Tana vuvvugar da fitsari da haila da nono, idan aka sha zuwa kwana biyu. Tana maganin kuturta. Tana amfani wajen rage majina. Ana dandaqata a zuba a wani qyalle a shaqa don maganin ciwon kai nan take, da mura. Shan ta da ruwa yana da amfani ga mai numfashij da qyar. Don haka tana matuqar taimakawa mai Asma. Hakanan mun tato sinadaranta mun zuba a wani magani mai suna (TASIRI DAGA ALLAH), don haka za ku iya neman wannan magani. ARRAIHAN/XOXXOYA Raihan tsiro ne mai qamshi, ana shuka shi a kudancin Asiya da Iran da wani vangare na Africa da tsakiyar America. Allah (S.W.T) yana cewa: " ﻓﺄﻣﺎ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻘﺮﺑﻴﻦ * ﻓﺮﻭﺡ ﻭﺭﻳﺤﺎﻥ ﻭﺟﻨﺔ ﻧﻌﻴﻢ " Amma wanda ya kasance daga cikin makusanta hutu da bishiyar Raihan da Aljanna sun tabbata a gare sh...

amfani da maganin tazarar haihuwa wato implan

  MAGANIN RIKICEWAR JININ HAILA : TAMBAYA TA 2282 ******************* Assalam, malam dan Allah sakaye sunana. Yaya aiki? Malam nice nake amfani da maganin tazarar haihuwa wato implan yanzu wata na hudu kenan, to kwanan nan se ya fara min wasa da al'ada ta, se nayi sati biyu ya dawo wannan karon kam ma bekai sati daya ba ya dawo, naga yadan zubo se kuma ban gani ba kuma a wannan rana ina azumi shin malam menene hukuncin sallah ta da azumi na? Shin wannan jini ya zama na ciwo ne ko kuma? Domin an bani magani a asibiti domin ya gyara min. Malam ayi hakuri zanso a tura min amsar ta nan. Nagode. AMSA ******* Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu. Su kwayoyi ko alluran tazarar haihuwa sukan yi kokarin chanza yanayin halittar Mace ne daga ainahin ginin farko wanda Ubangiji ya halicceta akansa. Don haka dole arika samun matsaloli marassa adadi. Mafiya yawan Matayen dake shiga wannan tsarin sai, sun sha fama da rikicewar jinin Al'ada. Wasu ma ciwuka da jinyoyi kala-kala a sassa...

Haila

  Haila Bayanin menene haila Kalmar (Haila) a larabci Tana nufin Kwararar wani abu da gudanar shi Ma’anar (Haila) a shari’a Wani jini ne da yake fita daga mahaifar mace, a wasu lokuta sanannu, ba tare da wani dalili ba. Siffar Yadda Jinin Haila Yake Baqi ne wuluk, kamar wanda aka qona, warinsa bai da daxi, mace tana jin xumi mai tsanani idan ya zo. Shekarun Fara Jinin Haila Babu wasu shekaru qayyadaddu na fara al’ada, wannan ya danganta ne da savanin xabi’ar mace da inda take rayuwa da yanayin wajen, don haka duk lokacin da mace ta ga jinin haila to haila ce. Tsawon Lokacin Haila Haila ba ta da wani lokaci, sananne, cikin mata akwai masu yin kwana uku, akwai masu kwana huxu. Galibin haila dai kwana shida ne ko bakwai, saboda faxin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ga Hamnatu ‘yar Jahshin – wanda ta kasance tana yin haila kwanaki masu yawa –  “Ki yi haila kwana shida, ko bakwai, da ilimin Allah, sannan ki yi wanka”  [Abu Dawud ne ya rawaito shi] Mas'aloli 1 - A qa'ida ma...