'YAN UWA, YAU QISSAR IMAMU ABU HANIFA (R) ZAN BA KU
Kowa ya san Imamu Abu Hanifa shi ne Limamin Fiqhu na farko a jerin Limaman Fiqhu guda hudu ma'abota Mazhabobin Fiqhu mafi shahara a Duniyar Muslunci.
Ya kasance a zamaninsa akwai wani babban Malamin Fiqhu kuma Alkali, wato Muhammad bn Abdirrahman Ibnu Abi Laila. Ya kasance Malamin Fiqhu ne amma Dan Makarantar ra'ayi ne ba Makarantar Hadisi ba.
To, Ibnu Abi Laila ya kasance a Masallaci yake zama yake yin alkalancinsa, wato a babban Masallacin Kufa. To an ruwaito cewa; wata rana bayan ya tashi daga alkalanci, har ya fita daga Masallacin sai ya ji wata mata tana ce ma wani mutum: "Ya dan Mazinata biyu (babansa da mamarsa)".
Wato ta nuna cewa; babansa mazinaci ne, mamarsa ma mazinaciya ce. To sai Alkali Ibnu Abi Laila ya sa aka kira ta. Sai ya koma Masallaci kan kujuran alkalancinsa ya zauna, sai ya yi mata Shari'a, ya yanke mata hukuncin kazafi saboda ba ta da shaidu hudu (4) a kan abin da ta fada. Sai ya sa aka yi mata haddin kazafi guda biyu, wato bulala dari da sittin (160), bulala tamanin a kan kazafi wa baban mutumin, bulala tamanin kuma a kan kazafi wa mamarsa.
To, sai labarin abin da ya faru ya riski Limamin Fiqhun Iraqi, wato Imamu Abu Hanifa, kawai sai Abu Hanifa ya ce: Wannan Alakilin ya tafka kurakurai guda shida (6) a cikin wannan hukunci:
1- Ya koma majalisin alkalanci bayan ya tashi, alhali bai kamata Alkali ya koma majalisin alkalanci bayan ya tashi ba.
2- Ya zartas da haddi a Masallaci, alhali Annabi (saw) ya yi hani a kan haka.
3- Ya yi bulala wa matar a tsaye, alhali su mata a zaune ake yi musu haddi, kuma cikin sutura da tufafi wadatacce.
4- Yi mata haddi har guda biyu, bulala 80 sau biyu, alhali idan mutum ya yi kazafi wa jama'a masu yawa cikin magana daya to haddi daya kawai za a yi masa.
5- Haka kuma ko da haddi biyun ne ya hau kanta to ba lokaci daya za a yi mata su ba, a'a, za a yi mata na farko, sai kuma a barta sai ta warke sai a zo a yi mata na biyun.
6- Ya tsayar da haddi a kan mai kazafin alhali masu hakkin kazafin ba su nemi hakan ba (wato ba su kawo kara ba).
Haba! ai da labari ya isa ga Alkali Ibnu Abi Laila kawai sai ya garzaya wajen Gwamnan Kufa ya ce masa: Akwai fa wani Matashi ana ce masa Abu Hanifa, yana kalu-balanta ta a cikin alkalancina, yana bayar da Fatawa sabanin hukuncin da na yanke, yana nuna cewa; ina yin kuskure a hukuncin nawa. Don haka ina so ka tsawatar masa don ya fita hanyata.
Sai kuwa Gwamna ya aika aka zo da Abu Hanifa, sai ya hana shi yin Fatawa gaba daya.
To sai ake ba da labarin cewa:
Wata rana Abu Hanifa yana gidansa tare da matarsa da dansa Hammadu da 'yarsa, sai 'yar tasa ta ce masa: Baba, ina Azumi, kuma jini ya fito daga tsakanin hakorana, amma na yi ta tofarwa har sai da yawuna ya dawo fari tas, gaba daya jinin ya dena fita. To shin Azumina zai karye idan na hadiyi yawun?
Sai Babanta Imamu Abu Hanifa ya ce mata:
سلي أخاك حمادا فإن الأمير منعني من الفتيا.
"Ki tambayi Dan uwanki Hammadu, saboda ni Gwamna ya hana ni yin Fatawa".
Duba cikin Littafin "Wafiyyaatul A'ayaan" na Ibnu Khallikan (4/ 180)
Allahu Akbar!
Lallai akwai darusa da ilmomi masu yawa a cikin wannar Qissah. Abin da ya ja hankalin Ibnu Khallikan daga cikinta shi ne:
Ka duba girman da'a ga Allah a umurninsa da ya yi na da'a ma Shugabanni, Abu Hanifa ya kasance hatta a sirrance a cikin gidansa tsakaninsa da iyalansa yana da'a ma shugabansa don kar ya saba umurnin Allah Madaukakin Sarkin.
Allah ya jikan Imamu Abu Hanifa ya yi masa gafara da rahama.
To jama'a, kun ga fa irin halin Faqaha'u Malaman Fiqhu magabata, suna da'a ma Shugabanninsu sau da kafa saboda da'a ma Allah Madaukaki.
A yau, da a ce: za a hana wani Malami yin Wa'azi ko bayar da Fatawa to da sai an tayar da zaune tsaye, alal akalli ko da a kafafen sadarwa ne.
All reactions:
77- Get link
- X
- Other Apps
Comments
Post a Comment