- Get link
- X
- Other Apps
SHAIKH JA'AFAR (R) DA 'YAN BOKO AQIDA A kokarinsu na batanci wa Marigayi Shaikh Ja'afar da Da'awarsa ta Sunna da mabiya Sunnan a yau, 'Yan Boko Aqida suna danganta shi da Marigayi Muhammad Yusuf wanda ya kafa Kungiyar Boko Haram, inda suke cewa; ai Muhammad Yusuf din almajirin Shaikh Ja'afar ne, don su nuna cewa; Muhammad Yusuf ya dauki tunanin Boko Haram ne daga Shaikh Ja'afar din. Alhali wasu da suka san Muhammad Yusuf kuma suka san Malam Ja'afar, sun tabbatar da cewa; asali Muhammad Yusuf tafiyar Harkar Gwagwarmayar kifar da Gomnati ya fara yi a karkashin jagorancin Ibrahim El- Zakzaky, wanda daga baya ya yi masa tawaye tare da sauran wadanda suka yi tawaye, bisa zargin shigar da Shi'anci cikin tafiyar, wadanda suka zama Kungiyar JTI, wacce take alakanta kanta da Kungiyar Ikhwan ta Misra. Wanda sai daga baya ne Muhammad Yusuf ya hadu da Malam Ja'afar a bisa tafiyar Sunna ko Salafiyya. A baya - bayan nan, tun bayan bayyanar wani faifan audio na...