Skip to main content

Posts

Showing posts from February, 2021

yadda ake yin man kwakwa

YADDA AKE YIN MAN KWAKWA Da kuma amfaninsa. Daga shafin Sunnah Medicine masu yin Ruq'yah da harhada Magungunan Musulunci. https://www.facebook.com/sunnahmedicinepage/ Lambar waya 08162600700, 08134434846. Yadda ake hada Man Kwakwa:- Ababe da za’a bukata •Kwakwa •Ruwa Yadda za a hada. A samu Kwakwa mai kyau, sai a 6are 6won a kankare bayan kwakwar ya rage farin kawai, sannan a yayyanka ta kanana saboda ta yi saukinmarkadawa. A zuba ruwa da dan dama a cikin blandar sai ahada da yankakkiyar kwakwar sai a markada har sai markaden ya yi laushi sosai. A sami a bin tatar kamu a tace ruwan kwakwarsosai, za a ga ruwan kamar madara. Za’a iya ajiye markadadden ruwan kwakwa nakwana daya ga wadda ba ta da firinji ko kuma asaka shi a firinji domin ruwan ya hadu sosai. Bayan kwana daya za a ga madarar kamarkindirmo a saman kwano. Sai a kwashe wannan madarar da aka tace a zuba ta a cikin tukunyar suyar sai a dora tukunyar a kan wuta, haka za a yi tajuyawa da cokali har sai wannan madarar ta komaka...

Gyaran jiki

GYARAN JIKI    DA SAURAN. MUHIMMAN ABUBUWA                                         *❐ KARIN HIP ❐* Idan kina Bukatar Hips Sannan kuma Mazaunan ki suyi Sutu sutu, Domin Hakan yana Kayatar da Mijin ki  ga abubuwan da zaa nema.  ♅ Madarar Shanu ♅ Zuma ♅ Dan kalin Turawa ♅ Coconba ♅ Kayan Marmari. ki samu dankalin turawa ki dafashi ya dahu sosai, idan yasha iski Hadashi da Cocoban dinki sai ki Marka deshi, ki dinga Sha da madarar shanu da Zuma kadan, Zaki Sha na tsawon wata 1. . Sannan ki dinga yawan Shan Mayan Marmari.          : ■ ・ KARFIN SHA"AWA ・■​ ➟ Zaki iya yin shayin kara karfin sha awa da ni ima yanda zakiyi shine kisamu sassaken baure ki dakashi saiki daka kanunfari ki hada da lefton kinasha zakiyi mamaki musamman idan ke matar aure ce…      :             ☐・ RAGE TUMBI​ ・☐ ➟ Mata da maza m...

Gyaran gashi

: ・ GYARAN GASHI ・  Muddin uwargida na kokarin gyaran gashi lokaci lokaci, za ta kiyaye gashin nata daga karairayewa, zai rika laushi kuma ya kara tsawo. Domin cimma wannan, za ki tanadi ganyen magarya, ki rika wanke da shi, yana kara karfafa gashi ya kuma hana shi zubewa. Ga wadansu daga cikin sinadaran da za ki tanada: 1. Man zogale. 2. Man kwakwa. 3. Man zaitun. Sai ki hade su guri guda ki rika shafawa a kanki a matsayin man kitson ki, ko kuma ki tanadi: 1. Danyen kwai sabulun salo 2. Sabulun salo 3. Garin shammar A fasa kwai, amma banda kwaiduwar farin kadai za ki yi amfani da shi, sai ki zuba sabulun salo a ciki, ki matse ki zuba garin shammar ciki sai ki wanke kai da shi. Allah ya taimake mu. Ga wani hadin kuma dai duk na gyaran gashi wannan hadin na masu karamin karfi ne domin abubuwan da za ki tanada ba za su fi karfin ki ba da farko za ki tanadi ruwan Tumatur ne da sabulun salo kawai za ki matse ruwan tumatir din sai ki zuba sabulun salon a ciki ki barshin ya samu tsayin m...

Amfanin hulba 21 ga lafiyar dan'adam

Amfanin Hulba Guda 21 Ga Lafiyar Dan-adam A wannan rana za mu kawo mu ku bayani dangane da amfanin Hulba ga lafiyar bil'adama. Hulba kamar yadda mu ka san ta, kalma ce ta larabci, da harshen turanci kuwa ana kiran ta da 'Fenugreek'. Hulba  wani tsiro ne mai matukar amfani ga lafiya, kuma shekaru aru-aru da su ka shude al'umma ke amfani da ita don samun waraka daga wasu matsalolin lafiya. Jama'a na amfani da ganye da kuma kwayar hulba wajen samar da magunguna tun a shekarun da su ka gabata.  Hulba ta shahara a kasashe da dama a duniya, sai dai anfi samun ta a wasu daga kasashen Larabawa musamman kasar Misra, sannan ana samun hulba a kasar Sin da kuma Indiya. A kasar Indiya su na kiran ta da, 'Methi' a yaren Hindu, a yaren Telugu na Indiyan kuwa su na kiran ta da 'Menthulu'. Wani bincike da wata kafar yada bayanai ta yanar gizo ta wallafa, ya nuna cewa, Hulba ta shahara a kasar Indiya saboda amfaninta ga lafiya, ta yadda za ka iya kiran ta gidan kowa d...

Alamomin ciwon sanyin mara na maza

DAN TAIMAKON JUNA DA MAGUNGUNAN DA MUKA SANI NA ISLAM: LAFIYA Alamomin Ciwon Sanyin Mara Na Maz Sanyin Mara Ciwon sanyi wata cuta ce wadda tafi yaduwa ta hanyar jima’i saboda su kwayoyin halittun da suke sanya cutar ana yada sune daga wannan mutum zuwa wancan mutum, ta jini, maniyyi, ruwan farji ko ruwan jiki. Alamomin ciwon sanyi ga maza sun sha banban tsakanin mutane wadanda suka riga suka kamu da cutar. Wannan kuma ya danganta ne da irin nau’in kwayar halittar cutar wacce ita ce take haddasa ciwon da kuma matakin da cutar ta takai a jikin mutum, wato wannan yana nufin, alamomi ko matakin farko da kamuwar cutar ko alamomi na gaba bayan ta dade da jimawa a jikin maras lafiyar.   samndaads Haka nan kuma, su ma yanayin alamomin sun sha banban ta fuskar tsanani ko kuma saukin su, koda kumada akwai rashin ganin alama ko daya duk da cewar, ko akwai cutar a jikin marar lafiyar. Maza da yawa na zargin suna da ciwon sanyi ne kawai a lokacin da suka ga wasu alamomi da basu saba da gani ba ...

Magungunan Musulunci Fitowa Ta farko

HABBATUS-SAUDA: Daga Nana A'isha (RA) ta ce: "Manzon Allah (SAW) ya ce: wannan Habbatus-Sauda waraka ce daga dukkan cuta sai dai mutuwa. FA'IDOJINTA: Idan aka damqata aka dama da zuma aka sha da ruwa mai zafi tana narkar da tsakuwar ciki. Tana vuvvugar da fitsari da haila da nono, idan aka sha zuwa kwana biyu. Tana maganin kuturta. Tana amfani wajen rage majina. Ana dandaqata a zuba a wani qyalle a shaqa don maganin ciwon kai nan take, da mura. Shan ta da ruwa yana da amfani ga mai numfashij da qyar. Don haka tana matuqar taimakawa mai Asma. Hakanan mun tato sinadaranta mun zuba a wani magani mai suna (TASIRI DAGA ALLAH), don haka za ku iya neman wannan magani. ARRAIHAN/XOXXOYA Raihan tsiro ne mai qamshi, ana shuka shi a kudancin Asiya da Iran da wani vangare na Africa da tsakiyar America. Allah (S.W.T) yana cewa: " ﻓﺄﻣﺎ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻘﺮﺑﻴﻦ * ﻓﺮﻭﺡ ﻭﺭﻳﺤﺎﻥ ﻭﺟﻨﺔ ﻧﻌﻴﻢ " Amma wanda ya kasance daga cikin makusanta hutu da bishiyar Raihan da Aljanna sun tabbata a gare sh...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊALAHI AHLIL ATHAR 10*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊALAHI AHLIL ATHAR 10* A yau mun san musɗalat kamar haka. 1. *Riwayatul Akaabir anil asagir( رواية الأكابر عن الأصاغر)* :Riwayar da manya suke samowa daga wanda basu kaisu ba a shekaru. 2. *Riwatul Abaa'i anil abna'i( رواية الآبآء عن الأبناء)*:  Riwayar da iyaye daga 'ya' yansu.Wasu kuma daga iyaye har zuwa kakanni. 3. *Almuhmal (المهمل)*:  Shi ne mutane biyu suyi riwaya daga mutum ɗaya kuma sunansu irin ɗaya. To in aka gano wanda yafi lizmtar malamin sai a rinjayar da Riwayar sa shi kuma ɗayan ya zama muhmal. 4. *Man haddasa wa nasiya(من حدث و نسي)*: Wanda ya bada hadisi ya manta ya bayar. In ya tabbatar bai bayarba sai a mayar da riwayar. In kuma yayi kokonto sai a karɓa. 5. *Musalsali (المسلسل)* : Hadisin da yazo da wata siffa iri ɗaya wacce taita maimaitawa a isnadinsa. Sai sigogin yadda ake karɓar riwaya. Wanda yaji shi kadai daga malamin sa zai ce  سمعت أو حدثني. Wannan itace sigar da tafi fitowa fili. Kuma tafi ɗaukaka.  Wanda yaji shida ...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 09*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 09* A yau mun san musɗalat kamar haka : 1. *Almarfu'u (المرفوع)*: Shi ne duk abin da aka danganta zuwa ga Annabi SAW na magana ko aiki ko tabbatar wa. 2. *Almauƙuuf(الموقوف)*:Shi ne duk abin da aka danganta zuwa ga Sahabi na magana ko aikinsa. 3. *Almaƙduu'u (المقطوع)*: Shi ne duk abin da aka danganta zuwa ga Tabi'i na magana ko aiki. ANA KIRIN MAUƘUF DA MAƘDU' ATHAR 4. *Almusnad(المسند)*: Shi ne hadisin da ya dangane ga Annabi SAW ba tare da yankewar isnadi ba. 5. *Al'aaliy- Al'luwwul Muɗlaƙ (العالي:العلو المطلق)* : Shi ne hadisi ya zo da mutane yan kaɗan in an gwada shi da wani wanda bashi ba. 6. *Al-aaliy Al'luwwul Nisbiy(العالي: العلو النسبي)*: Shi ne hadisin da ya zo da mutane kaɗan, zuwa ga ɗaya daga cikin manya malaman hadisi kamar shu'ubah. ULUWWUN NISBIY YA KASU GIDA GIDA 7. *Almuwafaƙah(الموافقة)*: Shi ne Isnadin mutum Y kai ga malamin ɗaya daga cikin malaman da suka rubuta littafin hadisi, kamar Bukhari k...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 08*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 08* A yau mun san musɗalat kamar haka: 1. *Majhulul Ayn(مجهول العين)*: Shi ne wanda mai riwaya guda ɗaya kawai ya ruwaito shi. 2. *Majhulul haal(مجهول الحال)*: Shi ne wanda mutane biyu ko fiye da haka suka yi riwaya a wajensa. Amma ba a ce amintacce ne a karɓi riwayarsa ba kuma shi ake cema Almastuur. 3. *Mai bidi'ah mufassiqa(المبتدع بدعة مفسقة)*: Shi ne mai riwaya ɗan bidi'ah amma bidi'ar da ke maida mutum mai saɓo. Malamai sunce ana iya karɓar hadisin sa matuƙar bai ruwaito abinda ke ƙarfafa bidi'arsa. 4. *Mai bidi'ah mukaffira(المبتدع بدعة مكفرو):* Shi ne mai riwaya ɗan bidi'a wacce ke maida mai ita kafiri. Kamar  bidi'ar cewa ƙur'ani halitta ne. Jumhurun malamai sun tafi akan cewa ba a karɓan riwayarsa haka Juzajaaniy malamin Nasa'i ya faɗa. 5. *Shaaz(الشاذ):* Riwayar mai mummunar hadda, a wajen wasu malamai. 6. *Mukhtaliɗ(المختلط):* Wanda lalacewar haddarsa bijiro wa tayi kamar saboda tsufa ko wata lalura....

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 07*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 07* A yau mun san musɗalaht kamar haka: 1. Mudrajul Isnaad(مدرج الإسناد): Shi ne hadisin da aka canza isnadinsa 2. Mudrajul Matn(مدرج المتن): Canza hadisin da aka danganta zuwa Sahabi zuwa ga wanda aka danganta zuwa ga Annabi  3. Al-maqlub(المقلوب): Shi ne hadisin da aka canza hadisi da kai gaba baya. 4. Al-mazid fi muttasilil asaneed(المزيد في متصل الأسانيد): Shi ne qara mutum a ruwaya. Kamar daga mutane biyar ya koma shida. 5. Almudɗarib(المضطرب): Shi ne canza isanadin wani hadisi da wani na daban. Akan yi hakan da gangan. 6. Almusahhaf da Almuharraf(المصحف و المحرف): Shi ne canza harafi ko digo ko wasali a hadisi. 7. Riwayatul Hadisi bil ma'ana(رواية الحديثباد بالمعنى):Baya halasta da gangan a canza lafazin hadisi saɓani yadda yazo sai ga Malami masani da cikakkiyar ma'anar hadisin 8. Idan hadisi yazo da kalmar da ma'anarta bata fito fili ba, sai ayi sharhin kalmar da bayanin abu da ke da ruɗarwaشرح الغريب و بيان المشكل. 9. Jahala(ا...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊALAHI AHLIL ATHAR 06*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊALAHI AHLIL ATHAR 06* A yau zamu san musɗalahat kamar haka: Ana gane Munƙadi'i idan aka gano masu ruwa basu haɗu ba akwai tazara tsakanin su. Shi yasa ake buƙatar sanin tarihi 1. *Mudallasi المدلس*: Shi ne hadisin da mai ruwaya ya tsallake malamin shi ya ambaci malamin malamin shi da lafazi mai ruɗarwa kamar: da 2. *Al-mursalul khafiyyi(المرسل الخفي)*: Shi ne mai ruwaya ya danganta hadisin sa ga wani malami da zamanin su ɗaya amma basu haɗu ba. Sannan game da suka ga me ruwaya takan kasance saboda: Ƙarya, Tuhumarsa da Ƙarya, mummunan kuskure, fasiƙanci, ruɗu, saɓama wanda suka fishi, rashin sanin waye shi, bidi'arsa, 3. *Maudu'i (الموضوع)*: Shi ne hadisin da aka yi Ƙarya aka danganta zuwa ga Annabi S. A. W 4. *Matruuki(المتروك)*: Hadisin wanda ake Tuhumarsa da ƙarya 5. *Munkari a wajen wasu malaman(المنكر على رأي)*: Hadisin mai mummunan kuskure, ko lalatacciyar hadda ko kuma fasiƙi. 6. *Al-Mu'allal(المعلل)*: Hadisin wanda ke da ruɗu, in akayi bibi...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 05*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 05* A yau zamu san musɗalat kamar haka: 1. *Al-muhkam(المحكم):* Shi ne hadisi ingantacce da ba wanda ya inganta yake cin karo dashi. 2. *Mukhtaliful hadis(مختلف الحديث):* Su ne hadisan da suke cin karo da juna a zahiri amma za a iya haɗa kansu ayi aiki dasu. 3. *Nasikh da Mansukh(الناسخ و المنسوخ):* Su ne hadisai guda biyu su ke cin karo da juna. Amma ɗaya na goge hukuncin ɗayan. Wanda aka fara faɗa shi ne Mansukh wanda aka faɗa daga baya shi ne Nasikh.  4. *Attarjeeh(الترجيح):* Shi ne a lokacin da hadisai suke cin karo da juna kuma ba a gano  wanda ya goge wani ba. Sai abi wasu qa'idoji domin rinjayar da wanda yafi ayi aiki dashi. 5. *Tawaqqufi(التوقف):* Shi ne a daka game da aiki da wasu hadisai lokacin da aka kasa gane wanda ya goge waniba. Kuma anbi qa'idoji na tarjeehi ba a samu yadda za ayi tarjeehinsa ba. 6. *Mu'allaq(المعلق):* shi ne hadisin da aka share isnadinsa daga farko ko kuma gaba dayansa aka ambaci Sahabi kawai. 7. *Mur...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 04*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 04* *قول الترمذي : حسن صحيح* *Lafazin da Tirmidhi yake cewa Hasanun Saheehun* Idan aka hada Lafazin guda biyu(حسن صحيح).  Ko dai mai ruwaya yana shakka ne(Kodai hadisin ya zama Hasanun ko ya zama Saheehi)  ko kuma ya lura da isnadi biyu ne (Isnadi ɗaya Hasan ne isnadi ɗayan kuma Saheehi). *زيادة راويهما مقبولة مالم تقع منافية لمن هو أوثق* *Ziyadul Thiƙah(ƙarin Amintacce a hadisi)*  Idan yayi ƙari ana karɓan ƙarin matuƙar bai sabama wanda ya fishi ba ana karɓa. Hadisin wanda yafi aminci (الثقة)sunansa ALMAHFUUZ (المحفوظ), shi kuma na wanda aka fi shi ake kira SHAZHI (الشاذ). Idan kuma mai rauni ya saɓa mawa ana kiran na amintaccen MA'ARUF (المعروف)shi kuma na mai raunin sunansa MUNKAR (المنكر). *Mutaba'ah:* Bibikon hanyoyin hadisai domin a samo ma hadisin FARD wanda zai goya masa baya. In aka samu FARD NISBY  ya samu irinsa yana goyon bayansa shi ake kira TABI'I (التابع). in kuma matani aka sama wanda yake kama dashi ana kiran sa...

fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 03*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSƊAHI AHLIL ATHAR 03* Hadisi maƙbuuli yakan fa'idantar da ilimi na nazari a maganar da tafi wajen malamai. Sannan sai hadisi gareebi, zata iya kasancewa a tushen isnadi ku kuma sabanin haka. Na farko shi ne Alfardul Muɗlaƙ, na  biyun shi ne Alfardul  nisbiy. Sharuddan Ingancin Hadeethi Aahaad 1. عدل الراوي: Adalcin mai riwaya 2. ضبط الراوي: Cikar haddar mai riwaya 3.  اتصال السند: Haduwar isanadi 4. خلوه من الشذوذ :Kubutarsa daga sabama sauran 5. خلوه من العللة: Kubutarsa daga aibi boyayye. Duk hadisin da ya cika sharuddan nan guda biyar shi ake cema Cikakken ingantaceصحيح لذاته.  A cikin nau'insa wank yafi wani daraja gwargwadon wanda yafi kiyaye sharuddan da kyau. Tuntuni ana gabatar da Saheehul Bukhaari, sai Muslim, sai wanda yazo bisa sharadinsu amma basu fitar dashi ba. In hadisi yazo daga wanda haddarsa bata cika ba, ana kiran hadisin da cikakken hadisi mai kyau الحسن لذاته.  In irin wannan yazo ta hanyoyi da yawa, ana kiransa Ingantac...

Fassarar *NUKHBATUL FIKR FI MUSDALAHI AHLIL ATHAR 02*

*NUKHBATUL FIKR FI MUSDALAHI AHLIL ATHAR 02* Muqaddimah: Yabo ya tabbata ga Allah da bai gusheba masani kuma mai iko. Allah yayi salati da aminci ga shugaban talikai S.A.W da alayensa da sahabbansa da wanda suka bisu da kyautatawa. Bayan haka, lalle rubuce rubuce a fannin Musdalahul hadeeth sun yawaita. Wasu sun fada, wasu kuma sun yawaita, wasu rubutun zube wasu a waqe. Daya daga cikin dalibai ya nemi da in rairayo masu wasu muhimman abubuwa daga cikin wanann ilimi. Sai na amsa ma roqonsa da fatan za a amfana. *Hadisi yana zuwa da ma'anoni guda hudu (الحديث ،السنة،الأثر،الخبر،النبأ)Duka ma'anarsu a dunqule yana nufin abinda aka danganta zuwaga Annabi S.A.W na magana ko aiki ko tabbatarwa.* Hadisi yana kasancewa kodai mutanen da ba adadi su ruwai to shi, ku mutane uku su ruwaito ko biyu, ko kuma mutum daya ya ruwaito shi. A. Wanda mutane suka ruwaito da yawa shi ake kira *ALMUTAWATIR المتواتر:* Shi ne hadisin da mutane da yawa suka ruwaito yawansu ya wuce su hada baki suyi qary...

Fassarar Nukhbatul Fikr ta ibn hajar 001

*نخبة الفكر في مصطلح أهل الأثر* *NUKBATUL FIKR NA IBN HAJAR 01* *ILIMIN MUSDALAHIL HADITH* ▪️Ma'anar Musdalahul HADITH ▪️Nasabarsa - Sunansa - Garinsu -Laqabinsa ▪️Haihuwarsa -▪️shekararsa da ya hadace Qur'ani - rasuwar mahaifinsa ▪️Tafiye tafiyensa na neman Ilimi - Garuwan da yaje  ▪️Littafansa ▪️Rasuwarsa ▪️Qwarewarsa da ilimin hadisi. Allah ya mana jagora ya bamu ikon saurara 01/09/1441

Hadisi da Sunna 007

*HADISI DA SUNNAH*   *(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*  Rubutun  Muhammad Abdullaah Assalafiy  _(Abu-Abdillaah)_   *Darasi na 07*   *SUNNAH A CIKIN HADISI*  A cikin Hadisai Sahihai Annabin Rahama _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya bayyana kyakkyawan matsayin da *Sunnah* take da shi a cikin addinin nan, ta yadda ba zai yiwu a yi shi ba sai da ita. A nan ga misalin guda ɗaya kawai daga cikinsu, kamar inda ya ce:   *Riwaya ta ɗaya:*  « أَلاَ إِنِّى أُوتِيتُ الْكِتَابَ وَمِثْلَهُ مَعَهُ ، أَلاَ يُوشِكُ رَجُلٌ شَبْعَانُ عَلَى أَرِيكَتِهِ يَقُولُ : عَلَيْكُمْ بِهَذَا الْقُرْآنِ ، فَمَا وَجَدْتُمْ فِيهِ مِنْ حَلاَلٍ فَأَحِلُّوهُ ، وَمَا وَجَدْتُمْ فِيهِ مِنْ حَرَامٍ فَحَرِّمُوهُ » « أَلاَ وَإِنَّ مَا حَرَّمَ رَسُولُ اللَّهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - مِثْلُ مَا حَرَّمَ اللَّهُ » Ku saurara! Haƙiƙa, an ba ni Alƙur’ani da wani misalinsa a tare da shi. Ku saurara! Ya yi kusa a samu wani mutum ƙosasshe a kan ...

Hadisi da sunnah 006

*HADISI DA SUNNAH*   *(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*  Rubutun  Muhammad Abdullaah Assalafiy  _(Abu-Abdillaah)_   *Darasi na 06*   *Aya ta uku:*  قُلۡ إِن كُنتُمۡ تُحِبُّونَ ٱللَّهَ فَٱتَّبِعُونِی یُحۡبِبۡكُمُ ٱللَّهُ وَیَغۡفِرۡ لَكُمۡ ذُنُوبَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورࣱ رَّحِیمࣱ  Ka ce: In kun kasance kuna son Allaah ne to ku bi ni. Allaah zai so ku kuma ya gafarta muku zunubanku. Kuma Allaah mai yawan gafara ne, mai yawan tausayi. _(Suratu Ali-Imraan: 31)._  Wannan Ayar ta nuna a fili cewa:  (i) Duk wata da’awa ta ƙaunar Allaah da mutum ya ke yi tana zama ta ƙarya ce kawai, kuma babu ko ƙanshin gaskiya a cikinta, matuƙar dai mai ita bai zama mabiyin Hadisi da Sunnah a fili ƙarara ba. (ii) Alamar son Allaah da Addinin Allaah Ta’aala shi ne a ga mutum yana bin Sunnah sak, kuma yana rabuwa da dukkan nau’o’in bidi’a.  (iii) Sakamakon bin Sunnah ga mutum shi ne: Samun ƙaunar Ubangiji ga bawa, kuma da samun gafarar zunub...

Hadisi da Sunnah 005

*HADISI DA SUNNAH*   *(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*  Rubutun  Muhammad Abdullaah Assalafiy  _(Abu-Abdillaah)_   *Darasi na 05*   *SUNNAH A CIKIN ALƘUR’ANI*  A cikin Ayoyi masu yawa na Alƙur’ani Allaah Mabuwayi Mai Girma ya bayyana matsayin Sunnah a cikin Musulunci, kamar inda ya ce:   *Aya ta ɗaya:*  وَأَنزَلۡنَاۤ إِلَیۡكَ ٱلذِّكۡرَ لِتُبَیِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَیۡهِمۡ وَلَعَلَّهُمۡ یَتَفَكَّرُونَ Kuma mun saukar da Alqur’ani a gare ka ne domin ka yi wa mutane bayanin abin da aka sassaukar musu, kuma domin ko sa riƙa yin tunani. _(Suratun Nahli: 44)._  Wannan aya ta nuna: (i) Babban aikin da Allaah _(Subhaanahu Wa Ta’aala)_ ya ɗora wa Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ shi ne yin bayanin Alqur’anin da ya saukar masa. (ii) Haƙiƙa! Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya bi wannan umurnin na Allaah _(Subaanahu Wa Ta’aala):_ Ya yi cikakken bayanin Alƙur’anin har n...

Akashe waya in za'a shiga masaallaci

 *DON ALLAH KU KASHE WAYA/KO KUSA A SILENT IDAN ZAKU SHIGA MASALLACI.* ``` "Na rasa me yake damun wasu daga cikin mutanen mu, idan zasu shiga masallaci domin yin sallah wasu daga cikinsu sukan manta basa kashe wayar su ko su sakata a silent, wasu kuma da gangan suke barinta a buɗe, ana kiransu za tayi ƙara ta ɗauki hankalin jama'a acikin masallaci"``` *"Irin waɗannan mutanen yana da matuƙar kyawu su fahimci cewa lallai fa shi masallaci ɗakin Allah ne, ba'a yin wasa acikin, sannan kuma ba'a ginashi face sai don ambaton Allah"* _"Bugu da ƙari shi masallaci guri ne na nutsuwa, duk wanda yake yin sallah sai wayarka tayi ƙara aciki ta ɗauki hankalinsa ai kaga ka ɗauki alhakinsa, domin ka shiga tsakanin ganawarsa da ubangijinsa Allah"_ "Ba shiga da waya cikin masallacin ne babu kyau ba, barin ta a kunne Bareda ansata a Silent ba tana ƙara kuma tana ɗaukar hankulan masallata shine babban laifin, ka kashe wayarka ko ka sakata a silent shine yafi z...

fassarar waqen ‎بداية السول في تفضيل الرسول صلى الله عليه وآله وسلم للشيخ العلامة العز عبد العزيز بن عبد السلام السلمي"

HIMMA BATA GA RAGO! Waƙe kenan na Littafin: "بداية السول في تفضيل الرسول صلى الله عليه وآله وسلم للشيخ العلامة العز عبد العزيز بن عبد السلام السلمي". Wanda wani ɗalibi cikin ɗalibai na Markazul Wa'ayil Islamiy Tudun Jukun Zaria, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Basheer Lawal Muhammad Zaria ya tsarasu a matsayin ta shi gudumuwar; don bada kariya ga Manzon tsira (S.A.W). Ɗalibi mai suna: Imrana Hamza 👳🏻‍♂️ 1. Ya wanda ba shi da kishiya,      Mata kaza ɗa bai da shi. 2. Shi ke da mulkin duniya,      Al'arshi shi ɗai ke da shi. 3. Tsira, Aminci, ɗaukaka,      Gun wanda babu awa ya shi. 4. Alai da matayensa duk,     Har mai biyar su ka sa da shi. 5. Ka daɗan basira Rabbana,      Waƙe na ɗan rera wa shi. 6. Shi ne ka aiko gunmu duk,     Ɗa'a ka ce mu yi yo ga shi. 7. Ka ba shi duk matsayan da ba,    Wani wanda yai dai dai da shi. 8. Ya zarce kowa duniya,      Har Lahira an san da shi. 9. Aike...

SAƘO ZUWA GA IYAYE!

SAƘO ZUWA GA IYAYE! Haƙiƙa al'amarin tarbiyyar yara musamman ƴaƴa mata, abu ne mai muhimmanci matuƙa, wanda da yawa a wannan lokacin mafi yawan iyaye suka yi sakaci ƙwarai a kan sa. Za ka samu yarinya ta fara girma ta kai shekara sha biyar 15, amma iyaye ba su damu da ina ta ke zuwa ba, yaushe ta ke dawowa makaranta ; da ƙawayen da ta ke mu'amala da su. Saboda haka, yana da kyau iyaye sun sanya idanu a kan ƴaƴansu musamman ƴaƴa mata. Akwai wasu shawarwari masu tsada da na tsara zan baiwa iyaye, domin katange ƴaƴansu daga maɓarnata: 1. Sanin waɗanda ƴaƴanku suke mu'amala da su a fili da kuma boƴe? 2. Sanya ido game da suturar da ƴar ku/ɗan ku suke sanyawa musamman lokacin da za su fita gida. 3. Hanasu kallon wasu tashoshin da ake yaɗa ɓarna da lalata tarbiyya. 4. Dakatar da ita daga fita gun saurayi da sunan soyayya, idan ba aurenta zai yi ba. 5. Sanya ido da bincike a cikin wayoyinsu, da kuma suwa suke mu'amala da su a wayar. 6. Lura da lokacin da suke kwanciya barci da...

*_▪️📖♦️ DAGA DAUSAYIN ALƘUR'ANI MAI GIRMA 24 ♦️📖▪️_*

*_▪️📖♦️ DAGA DAUSAYIN ALƘUR'ANI MAI GIRMA 24 ♦️📖▪️_* *_✍️ Yusuf Lawal Yusuf_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ_* إِذَا جَاءَ نَصْرُ اللَّهِ وَالْفَتْحُ ( ١) وَرَأَيْتَ النَّاسَ يَدْخُلُونَ فِي دِينِ اللَّهِ أَفْوَاجًا (٢) فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَاسْتَغْفِرْهُ إِنَّهُ كَانَ تَوَّابًا (٣) النصر: (١-٣). 1. Idan nasarar Allah ta zo da kuma buɗe (Makka). 2. Ka kuma ga mutane suna shiga cikin addinin Allah ƙungiya-ƙungiya. 3. To ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka, ka kuma nemi gafararsa. Lalle Shi Ya kasance Mai karɓar tuba ne. Suratun Nasri (1-3). *_Tafsiri:_* Allah (Subhanahu Wata'ala) ya buɗe Surar da yi wa Manzonsa (sallallahu alaihi wa sallama) albishir da samun gagarumar nasara da buɗe garin Makka, sannan zai ga mutane ƙungiya-ƙungiya suna ta shiga addinin Musulunci bayan a da suna gaba da shi. An karɓo daga Abu Huraira (radiyallahu anhu) ya cw: Lokacin da wannan Surar ta sauja, sai Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallama) ya ce: "Mutanen Yaman sun zo, mas...

Hadisi da Sunnah 003

*HADISI DA SUNNAH*   *(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*  Rubutun  Muhammad Abdullaah Assalafiy  _(Abu-Abdillaah)_   *Darasi na 03*   *SUNNAH DAIDAI DA ALƘUR’ANI TA KE*  Sanannen abu ne a wurin dukkan *Ahlus-Sunnah* cewa Alƙur’ani maganar Allaah ne, saukakke daga wurinsa ba halitacce ba ne, wanda kuma Allaah ya bautar da bayi da karatunsa. Shi wata wanzajjiya kuma tabbatacciyar mu’ujiza ce da ta gagari dukkan halittu a kan su zo da irinta!  Ta wannan fuskar Alƙur’ani a sama ya ke, kuma ya fi falala da daraja a kan dukkan maganganun da ba shi ba, har da Sunnar Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)._  Amma ta fuskar kafa hujja ko fitar da dalili a kan wani hukuncin shari’ah, Sunnah Sahihiya daidai ta ke da Alƙur’ani, babu fifiko a tsakaninsu. Domin dai dukkansu wahayi ne daga wurin Allaah Maɗaukakin Sarki wanda ya faɗa game da Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam):_  وَمَا یَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰۤ ....

Hadisi da Sunnah 002

*HADISI DA SUNNAH*   *(A Fahimtar Ahlus-Sunnah Salafiyyah)*  Rubutun  Muhammad Abdullaah Assalafiy  _(Abu-Abdillaah)_   *Darasi na 02*   *1. MA’ANAR SUNNAH*  Asali a cikin harshen Larabci idan aka ce: *Sunnah* to kawai ana nufin: Hanya ko matafiya, kyakkyawa ko mummuna. Kamar maganar Manzon Allaah _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ cewa:  « مَنْ سَنَّ فِى الإِسْلاَمِ سُنَّةً حَسَنَةً فَلَهُ أَجْرُهَا وَأَجْرُ مَنْ عَمِلَ بِهَا بَعْدَهُ ، مِنْ غَيْرِ أَنْ يَنْقُصَ مِنْ أُجُورِهِمْ شَىْءٌ ، وَمَنْ سَنَّ فِى الإِسْلاَمِ سُنَّةً سَيِّئَةً كَانَ عَلَيْهِ وِزْرُهَا وَوِزْرُ مَنْ عَمِلَ بِهَا مِنْ بَعْدِهِ ، مِنْ غَيْرِ أَنْ يَنْقُصَ مِنْ أَوْزَارِهِمْ شَىْءٌ » Duk wanda ya sunnata wata kyakkyawar Sunnah a cikin musulunci, to yana da ladanta da ladan duk wanda ya yi aiki da ita a bayansa, ba tare da wani abu na ladaddakinsu ya ragu ba. Haka kuma duk wanda ya sunnata wata mummunar Sunnah a cikin musulunci, to yana da zunubinta da zu...